Shafukan sada zumunta na da hadari ga lafiyar matasa – Masana

Date:

Wani babban jami’in lafiya a kasar Amurka ya fitar da gargadi kan hadarin shafukan sada zumunta ga yara da matasa.

Dr Vivbek Murthy, wanda shi ne shugaban ma’aikatar lafiya ta Amurka ya ce kafofin sada zumunta da muhawara da kananan yara da matasa ke amfani da su na haifar da manyan kalubale ga lafiyar jiki da rayuwarsu.

Sannan suna haddasa matsalar rashin cin abinci da jefa masu amfani da su cikin damuwar rashin yarda da kai.

BBC Hausa ta rawaito Rahoton ya ce matakan da ake dauka domin rage damar da yara ke da ita ko matasa a shafukan sada zumunta ba sa aiki.

Sannan kuma akwai sauran jan aiki a binciken gano cikakken tasirin da wadannan shafuka ke yi a rayuwar matasa.

Sai dai kuma duk da wannan gargaɗi masanin ya ce akwai wasu alfanu da waɗannan shafuka kan yi ga wasu rukuni na mutane a rayuwa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...