Isa Bello Ja ya bayyana abubuwan da yan Nigeria za su yi don Tinubu ya magance matsalolin Nigeria

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

Guda cikin dattawan kasar na Alhaji Isa Bello ja ya bukaci al’ummar Nigeria da su kyautata zato ga sabuwar gwamnati domin samun ingantacciyar rayuwa ga al’umma ƙasar nan baki daya.

 

” Babu shakka sabon zaɓaɓɓen shugaban ƙasa Bola Tinubu yana da kwarewa a al’amuran da ya shafi Shugabanci, don haka muke yi masa kyakyawan zato”.

Alhaji Isa Bello Ja ya bayyana hakan ne lokacin da yake ganawa da jaridar kadaura24 a Kano.

Auren dole: Wata Matashiya ta yi karar Mahaifinta a kotu

” Ya yi Gwamnan Jihar Lagos kuma shi ya dora jihar a tafarki na cigaba har ta kai yadda take a halin yanzu, ya inganta tattalin arziki jihar fiye da na kowacce jiha a Nigeria, to haka muke tsammani zai yiwa Nigeria”. Inji Shi

Alhaji Isa Bello Ja wanda ake yi masa lakabi da Dattijon arziƙi yace yana da kwarin gwiwar matsalolin Nigeria zasu kadau idan al’ummar Nigeria suka dage da yiwa sabon zaɓaɓɓen shugaban ƙasa addu’o’in samun nasara.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...