Yaƙin Sudan: Yadda aka bar wasu daliban Najeriya a Sahara cikin mawuyacin hali

Date:

Daga Umar Sani Kofar Na’isa

 

Wasu daliban Najeriya da ke kan hanyar su ta guduwa daga ƙasar Sudan sakamakon tashe tashen hankula sun makale Sahara a ranar Alhamis.

 

Bayan amince da tsagaita wuta na kwanaki uku da dakarun Sudan da dakarun yan tawayen kasar suka cimma, kasashen na ci gaba da kokarin kwashe ‘yan kasarsu.

Yakin Sudan: An kaiwa daliban Nigeria hari

A ranar Larabar da ta gabata ne gwamnatin Najeriya ta ce ta saki kudi kimanin Naira Miliyan 150 domin daukar hayar motocin bas guda 40 don jigilar wasu ‘yan Najeriya daga Sudan zuwa birnin Alkahira na kasar Masar, inda za a kai su yan Najeriyan.

Yanzu Yanzu: Shugaba Buhari ya halarci Faretin Sojoji Sanye da kakin Soji

Amma wasu daga cikin daliban da aka kwashe sun bayyana cewa suna cikin mawuyacin hali akan hanyarsu ta zuwa kasar ta masar.

Wata daliba da abin ya shafa, wadda ta nemi a sakaye sunanta ta , ta ce direbobin sun sha alwashin ba za su karasa da su kasar masar din ba, har sai an kammala biyansu kudaden da aka yi yarjejeniya da su.

 

“Kafin mu fara wannan tafiya, mun fuskanci abubuwa daban-daban, yanzu haka maganar da nake yi maka mun makale a cikin wata sahara tsawon awanni 5, ba mu san ma Inda muke ba.

“Ba mu da ruwa, Kudinmu ya kare, kuma Direbobin sun ce baza su motsa ko ina da motocin ba,har sai an cika musu kuɗin su dinsu. Mun makale a cikin jeji. Ba mu da komai. Ba mu ma san inda muke ba, kuma muna cikin babban hatsari.”

Sai dai Abike Dabiri-Erewa, shugaban hukumar ‘yan Najeriya mazauna kasashen waje (NiDCOM), ta ce an shawo kan matsalar kuma an ci gaba da aikin kwashe mutanen.

Kimanin ‘yan Najeriya 5,500 ne da suka hada da dalibai suka makale a birnin Khartoum da wasu garuruwan Sudan sakamakon rikicin da ya barke a kasar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kotu a Kano ta hukunta masu shago saboda zubar da shara a kan titi

Kotun tafi da gidanka da ke Kano ta yanke...

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama mata da maza da ke aikata badala

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama mata hudu...

Hukumar Kula da Gidajen Gyaran Hali ta Magantu Kan Batun Sheikh Abduljabbar

Hukumar Gyaran Hali ta Jihar Kano ta bayyana cewa...

Dalilin da ya sa na bar tafiyar Kwankwasiyya – Farouk Lawan

Tsohon ɗan majalisar tarayya, Farouk Lawan, ya bayyana cewa...