Gwamnatin tarayya ta dakatar da cire tallafin man fetur

Date:

Daga Auwalu Alhassan Kademi

 

Majalisar kula da tattalin arziƙin Najeriya ta ce ba yanzu ne lokacin da ya dace a cire tallafin man fetur ba a ƙasar.

 

Ministar Kuɗi da tsare-tsare ta ƙasa Zainab Ahmed ce ta bayyana hakan bayan kammala taron Majalisar da aka yi a ranar Alhamis, wanda mataimakin Shugaban Najeriya Yemi Osinbajo ya jagoranta a fadar gwamnati.

 

Ta ce za a ci gaba da dukkan ayyukan da aka fara game da shirin cire tallafin na tuntubar jihohi da sauran masu ruwa da tsaki, ciki har da wakilan sabuwar gwamnati mai jiran gado.

Yakin neman zabe: APC ta soke zuwan Tinubu Kano

“Majalisar ta amince da cewa dole ne a cire tallafi na farko cikin gaggawa ba tare da wani ɓata lokaci ba, domin kuwa ba abu ne mai ɗorewa ba”. A cewar Zainab shamsuna

 

“Ba za mu iya ci gaba da biya ba. Dole mu kalli yadda cire tallafin ba zai jefa rayuwar ‘yan Najeriya ba cikin mawuyacin hali.

“Akwai buƙatar neman mafita bayan cire tallafin muna buƙatar yin shiri game da hakan domin tabbatar da an taimaka wa mutane da cire tallafin zai shafa.”

Gwamnatin Najeriya ta ce ta karɓo aron dalar Amurka miliyan 800 daga Bankin Duniya domin sassauta wa mutane raɗaɗin cire tallafin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...