Gwamnatin tarayya ta dakatar da cire tallafin man fetur

Date:

Daga Auwalu Alhassan Kademi

 

Majalisar kula da tattalin arziƙin Najeriya ta ce ba yanzu ne lokacin da ya dace a cire tallafin man fetur ba a ƙasar.

 

Ministar Kuɗi da tsare-tsare ta ƙasa Zainab Ahmed ce ta bayyana hakan bayan kammala taron Majalisar da aka yi a ranar Alhamis, wanda mataimakin Shugaban Najeriya Yemi Osinbajo ya jagoranta a fadar gwamnati.

 

Ta ce za a ci gaba da dukkan ayyukan da aka fara game da shirin cire tallafin na tuntubar jihohi da sauran masu ruwa da tsaki, ciki har da wakilan sabuwar gwamnati mai jiran gado.

Yakin neman zabe: APC ta soke zuwan Tinubu Kano

“Majalisar ta amince da cewa dole ne a cire tallafi na farko cikin gaggawa ba tare da wani ɓata lokaci ba, domin kuwa ba abu ne mai ɗorewa ba”. A cewar Zainab shamsuna

 

“Ba za mu iya ci gaba da biya ba. Dole mu kalli yadda cire tallafin ba zai jefa rayuwar ‘yan Najeriya ba cikin mawuyacin hali.

“Akwai buƙatar neman mafita bayan cire tallafin muna buƙatar yin shiri game da hakan domin tabbatar da an taimaka wa mutane da cire tallafin zai shafa.”

Gwamnatin Najeriya ta ce ta karɓo aron dalar Amurka miliyan 800 daga Bankin Duniya domin sassauta wa mutane raɗaɗin cire tallafin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kotu a Kano ta hukunta masu shago saboda zubar da shara a kan titi

Kotun tafi da gidanka da ke Kano ta yanke...

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama mata da maza da ke aikata badala

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama mata hudu...

Hukumar Kula da Gidajen Gyaran Hali ta Magantu Kan Batun Sheikh Abduljabbar

Hukumar Gyaran Hali ta Jihar Kano ta bayyana cewa...

Dalilin da ya sa na bar tafiyar Kwankwasiyya – Farouk Lawan

Tsohon ɗan majalisar tarayya, Farouk Lawan, ya bayyana cewa...