Kifewar kwale-kwale ta yi sanadiyyar Rasuwar Mutane 5 a Kano

Date:

Daga Aisha Aliyu Umar

 

Hukumar kashe gobara ta jihar Kano a ranar Lahadin da ta gabata ta tabbatar da mutuwar mutane biyar yayin da wasu shida suka tsira daga hatsarin kwale-kwale a Dam Kanwa da ke karamar hukumar Madobi .

 

Kakakin hukumar, Saminu Abdullahi, ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na Najeriya a wata tattaunawa ta wayar tarho yace wani Umar Faruk-Dalada, ne ya sanar da su labarin halin da ake ciki da kuma inda ya faru.

Hutuna: Yadda Sarkin Kano ya gudanar da Hawan Nasarawa

Ya ce: “Lamarin ya faru ne a ranar 22 ga Afrilu, da misalin karfe 05:40 na yamma.

 

“Akwai mutane 11 a cikin kwale-kwalen, an ceto shida yayin da guda biyar kuma suka rasa rayukansu.

Sunayen wadanda suka rasa rayukansu a hatsarin sun hada da Abdulrazak Nabara mai shekaru 40; Dalha Muktar-Atamma, 40; Mustapha Ibrahim, 45; Umar Isah mai shekaru 35 da Umar Idris mai shekaru 35,” inji shi.

ya ce wadanda abin ya shafa sun fito ne daga karamar hukumar Fagge ta jihar kano.

Ya ce an fara gudanar da bincike kan hatsarin kwale-kwalen kuma za a sanar da musabbabin faruwar lamarin da zarar an kammala bincike.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...