Bayan kwanshe makonni a waje, yau Tinubu zai dawo Nigeria,

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

A Yau Litinin ne ake sa ran zaɓaɓɓen shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu zai dawo gida Nigeria.

 

Tinubu zai koma Najeriya ne bayan ya shafe tsawon mako biyar a Paris, inda ya huta, bayan kammala yaƙin neman zaɓen da ya ba shi nasara.

Kifewar kwale-kwale ta yi sanadiyyar Rasuwar Mutane 5 a Kano

Tun farko an tsara cewa zaɓaɓɓen shugaban na Najeriya zai kwan biyu a Paris cikin ƙasar Faransa, daga nan kuma ya wuce zuwa birnin London, kafin ya dangana da ƙasar Saudiyya.

 

Sai dai rashin ganin sa a ƙasar Saudiyya lokacin aikin umra, musamman daidai lokacin da shugaban ƙasar mai barin gado, Muhammadu Buhari yake can, ya haifar da jita-jita da raɗe-raɗi.

Wani mataimakinsa na musamman Bayo Onanuga ne ya tabbatar da rahoton komawar Tinubun Najeriya, ko da yake bai cewa ga taƙamaimai lokacin da zai sauka a ƙasar ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...