An haramtawa limamai karanta Qur’ani daga wayar hannu a lokacin Tarawi da Tahajjud

Date:

Daga Aisha Aliyu Umar

 

Ma’aikatar kula da harkokin addinin Musulunci da wakafi ta kasar Kuwait ta bayyana haramta wa limamai karanta Alƙur’ani daga wayoyinsu na hannu a lokutan sallolin nafilfilun dare na watan Ramadana.

 

Jaridar Al-Rai ta ruwaito cewa hakan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da ta samu sa hannun ƙaramin minista mai kula da harkar masallatai, Salah Al Shilahi.

 

Goman ƙarshe: Ya kamata matasa ku kashe Datar wayoyin ku, ku daina kallon TV – Dr. Ali Tamasi

Sanarwar ta ƙarfafa wa limamai gwiwa da su riƙa amfani da haddarsu ta Ƙur’ani a lokutan sallolin Tarawihi da Tahajjud, kasancewar su (limaman) misali ne ga sauran al’umma.

Ƙasar Ingila za ta dakatar da daukar ma’aikatan kiwon lafiya daga Najeriya

Ta ƙara da cewa ya kamata kowane limami ya yi muraji’ar karatunsa yadda ya kamata gabanin jan sallah a maimakon karantowa daga cikin waya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Hukumar almajirai da yaran da ba sa zuwa Makaranta ta kaddamar da yi wa yaran da ba sa zuwa Makaranta Rijista a Kano

Daga Saminu Ibrahim Magashi   Hukumar kula da almajirai da yaran...

Da gudu zan karɓi tayin kujerar mataimakin shugaban ƙasa – Barau Jibrin

Daga Isa Ahmad Getso Mataimakin shugaban Majalisar Dattawan Najeriya, Sanata...

Inganta tsaro: Shugaban K/H Tarauni ya ba da fili domin gina ofishin Civil Defence a karkasara

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Shugaban karamar hukumar Tarauni, Alhaji Ahmed...

Gwamnan Kano ya yi sabbin nade-nade

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya nada Malam...