Aikin titin Abuja-Kaduna-Kano ba zai kammala a gwamnatin Buhari ba- Fashola

Date:

Daga Al-Ameen Sa’eed Bichi

Babantunde Raji Fashola Ministan ayyuka da Gidaje, ya bayyana cewa aikin gina titin Abuja zuwa Kaduna zuwa Kano zai wuce wa’adin mulkin gwamnatin shugaba Muhammadu Buhari da zata kare nan da 29 ga watan mayu.
Sai dai kuma Fashola, wanda ya bayyana haka a yayin ziyarar duba aikin gadar Loko-eweto a jihar Nasarawa a ranar Laraba, ya ce za a kammala titin Legas zuwa Ibadan a ranar 30 ga Afrilu.
A cewar Fashola, titin Abuja-Kaduna-Kano ya kasance mafi girman dukkan ayyukan titin ta fuskar girma da kuma kudi da gwamnatin Buhari ta bayar.
“Abuja-Kano ita ce mafi girma a cikin ayyuka uku ta fuskar girma, ta fuskar kasafin kudi; shi ne kilomita 375.
“Ya ƙunshi gadoji 41 masu girma daban-daban. Shi ne na ƙarshe don farawa, don haka ba zai iya gamuwa a lokaci guda ba. Wannan ita ce magana ta gaskiya.
“Amma mun samu ci gaba daga Zariya zuwa Kano, wato kilomita 137, kuma ‘yan kwangilar sun shaida mana cewa ya zuwa ranar 15 ga watan Mayu za a kammala aikin.
“Sai kuma muna da Kaduna zuwa Zariya, mai nisan kilomita 70 da wani abu. Shi ma wannan bangaren, sun ce za a kammala shi a ranar 30 ga wannan wata, kuma za a bude su baki daya domin al’umma su ci gaba da amfani da su,” inji shi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin Sarautar Kano: Fadar Sarki Sanusi ta zargi magoya bayan Sarki Aminu Ado Bayero da kai farmaki Kofar Kudu

Daga Sani Idris Maiwaya   Rikicin Masarautar kano ya na neman...

Shugabannin Kasuwar Kanti Kwari sun shiryawa Gwamnan Kano Addu’o’i na musamman

Daga jafar adam Shugaban kasuwar Kantin Kwari Sharu Abdullahi Namalam...

Dalilin Kwankwaso na kin shiga Hadakar ADC

Jam'iyyar NNPP ta ce abin da ya sa ba...