Aikin titin Abuja-Kaduna-Kano ba zai kammala a gwamnatin Buhari ba- Fashola

Date:

Daga Al-Ameen Sa’eed Bichi

Babantunde Raji Fashola Ministan ayyuka da Gidaje, ya bayyana cewa aikin gina titin Abuja zuwa Kaduna zuwa Kano zai wuce wa’adin mulkin gwamnatin shugaba Muhammadu Buhari da zata kare nan da 29 ga watan mayu.
Sai dai kuma Fashola, wanda ya bayyana haka a yayin ziyarar duba aikin gadar Loko-eweto a jihar Nasarawa a ranar Laraba, ya ce za a kammala titin Legas zuwa Ibadan a ranar 30 ga Afrilu.
A cewar Fashola, titin Abuja-Kaduna-Kano ya kasance mafi girman dukkan ayyukan titin ta fuskar girma da kuma kudi da gwamnatin Buhari ta bayar.
“Abuja-Kano ita ce mafi girma a cikin ayyuka uku ta fuskar girma, ta fuskar kasafin kudi; shi ne kilomita 375.
“Ya ƙunshi gadoji 41 masu girma daban-daban. Shi ne na ƙarshe don farawa, don haka ba zai iya gamuwa a lokaci guda ba. Wannan ita ce magana ta gaskiya.
“Amma mun samu ci gaba daga Zariya zuwa Kano, wato kilomita 137, kuma ‘yan kwangilar sun shaida mana cewa ya zuwa ranar 15 ga watan Mayu za a kammala aikin.
“Sai kuma muna da Kaduna zuwa Zariya, mai nisan kilomita 70 da wani abu. Shi ma wannan bangaren, sun ce za a kammala shi a ranar 30 ga wannan wata, kuma za a bude su baki daya domin al’umma su ci gaba da amfani da su,” inji shi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...