Dakatar da gine-gine: Ka jira a rantsar da kai kafin ka fara bada umarni – Ganduje ya fadawa Abba Gida-gida

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Gwamnatin Kano ta yi kira ga zaɓaɓɓen gwamnan jihar Injiniya Abba Kabir Yusuf ya yi haƙuri, ya daina baiwa al’ummar jihar kano umarnin da sunan shawara ga jama’a, Saboda irin wannan shawara za ta iya haddasa ruɗani na babu gaira babu dalili a cikin jihar.

Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da kwamishinan yaɗa labarai na jihar kano, Muhammad Garba ya fitar don maida martani ga zaɓaɓɓen gwamnan a kan batun dakatar da gine-gine a wurare mallakin gwamnatin kano.
Idan za’a iya tunawa kadaura24 ta rawaito cewa zaɓaɓɓen gwamnan kano Injiniya Abba Kabir Yusuf ya baiwa Masu gine-gine a wuraren gwamnatin shawarar su dakatar da hakan ko kuma duk abun da ya biyo baya su yi kuka da kansu.
Gwamnatin Kano ta ce abin da zaɓaɓɓen gwamnan ya yi na bayar da umarni kan abun da hurumi ne na gwamnatin ba dai-dai bane, saboda har yanzu Dr  Abdullahi Umar Ganduje sh ne gwamnan jihar gar ranar 29 ga watan mayu wanann shekara ta 2023.
Ta ƙara da cewa kamar yadda yake ƙunshe a cikin tsarin mulkin Najeriya, Dr. Abdullahi Umar Ganduje zai ci gaba da zama gwamna mai cikakken iko har zuwa ranar 29 ga watan Mayu, kuma yana da damar gudanar da ayyukansa hatta a ranar jajiberen saukarsa daga mulki.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Sarkin Kano na 15 ya gana da Shugaba Tinubu kan rikicin Rimin Zakara

    Mai Martaba Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado...

Da dumi-dumi: Tinubu ya baiwa sakataren jam’iyyar APC na Kano mukami

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Sakataren jam’iyyar APC na jihar Kano,...

Gwamnatin Kano ta haramtawa yan kwangila zuwa ma’aikatar kananan hukumomi ta jihar – Kwamishina

Gwamnatin kano ta ja kunnen yan kwangilar ayyukan kananan...

Iftila’i: Almajirai 17 sun kone kurmus 15, sun jikkata sanadiyya wata gobara

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Wata gobara da ta tashi ta...