Ɗan takarar APC, Namadi ya lashe zaɓen gwamna a Jigawa

Date:

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa, INEC ta bayyana Umar Namadi na jam’iyyar APC a matsayin wanda ya lashe zaben gwamnan jihar Jigawa.

 

Jami’in zaben, Farfesa Umar Zaiyan na Jami’ar Tarayya ta Birnin Kebbi ne ya sanar da sakamakon zaben a jiya Lahadi a Dutse.

 

Zaiyan ya ce Namadi ya samu kuri’u 618,449 inda ya doke abokin hamayyarsa Mustapha Sule Lamido wanda ya samu kuri’u 368,726.

 

Ya ce: “Ni Farfesa Umar Zaiyan na tabbatar da cewa Umar Namadi na jam’iyyar APC, bayan ya cika sharuddan doka an ayyana shi a matsayin wanda ya lashe zaben gwamnan Jigawa.”

 

A cewarsa, mutane miliyan 1.07 aka tantance a zaben na ranar 18 ga watan Maris da kuri’u miliyan 1.05, daga cikin kuri’u miliyan 1.03 da aka kada a zaben.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...