Ɗan takarar APC, Namadi ya lashe zaɓen gwamna a Jigawa

Date:

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa, INEC ta bayyana Umar Namadi na jam’iyyar APC a matsayin wanda ya lashe zaben gwamnan jihar Jigawa.

 

Jami’in zaben, Farfesa Umar Zaiyan na Jami’ar Tarayya ta Birnin Kebbi ne ya sanar da sakamakon zaben a jiya Lahadi a Dutse.

 

Zaiyan ya ce Namadi ya samu kuri’u 618,449 inda ya doke abokin hamayyarsa Mustapha Sule Lamido wanda ya samu kuri’u 368,726.

 

Ya ce: “Ni Farfesa Umar Zaiyan na tabbatar da cewa Umar Namadi na jam’iyyar APC, bayan ya cika sharuddan doka an ayyana shi a matsayin wanda ya lashe zaben gwamnan Jigawa.”

 

A cewarsa, mutane miliyan 1.07 aka tantance a zaben na ranar 18 ga watan Maris da kuri’u miliyan 1.05, daga cikin kuri’u miliyan 1.03 da aka kada a zaben.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Zargin Almundahana: ICPC zata gurfanar da shugaban hukumar zabe ta Kano da wasu mutum biyu

    Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta (ICPC)...

Dalilin da ya hana ni zuwa Kano tarbar Tinubu – Ganduje

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Tsohon shugaban jam’iyyar APC na kasa,...

Shugaban RATTAWU na Kano ya taya sabbin shugabannin kungiyar na kasa murna

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Shugaban kungiyar ma’aikatan rediyo, Talabijin da...

Dalilina na ziyartar gwamnan Kano Abba – Inuwa Waya

Daga Rahama Umar Kwaru Tsohon Wanda ya nemi Zama Dan...