Sha’aban Sharaɗa ba takarar gaske yake ba, shi yasa na bar shi – Rarara

Date:

Daga Maryam Ibrahim Zawaciki

 

Shahararren mawakin nan Dauda Kahutu Rarara ya ce, duk da shi ya tsayar da Sha’aban Ibrahim Sharaɗa takarar Gwamna, amma ya ɗauka da gaske yake kafin daga bisani ya gano ta wasa ce.

 

Rarara ya bayyana hakan hira da Jaridar Intanet ta DCL Hausa inda ya zargi Sha’aban da shinshinar PDP a zaɓen Shugaban ƙasa da ya gabata maimakon APC da suka yi yarjejeniya.

Karanta: 2023: Idan na zama gwamnan kano Zan baiwa kananan hukumomi ‘yankin cin gashin kansu – Gawuna

 

” Ni na tsayar da Sha’aban takarar gwamnan na yake yi, ya zo ya same yace yana so yayi takarar gwamnan Kano kuma gashi duk jam’iyyun sun tsayar da yan takara, ni da wasu mutane da ba sai na fadi sunansu mu muka je muka Nemo masa jam’iyyar ADP domin yayi takara a cikin ta, don haka duk wata maganar takarar Sha’aban ni nasan ta Kuma na bar shi ne saboda na fahimci ba takarar gaske yake ba”. Inji Rarara

 

Karanta: NNPP ta kori mataimakin dan takarar gwamna, da wasu daga cikin Shugabannin Jam’iyyar

” A cikin Mutane dubu daya da suke tare da Sha’aban dari bakwai ni na kawo su ko kuma wadanda na kawo su suka kawo su, don haka ni na tsayar da shi takarar Kuma bar shi ne saboda na fahimci ba takarar gaske yake ba “.

 

 

A cikin hirar Rarara ya bayyana cewa Nasiru Gawuna yafi kowanne dan takarar gwamnan kano chanchanta Saboda nagartar da yake da ita da Kuma yadda ya mika lamarin takarar sa ga Allah .

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...