Daga Rukayya Abdullahi Maida
Mataimakin gwamnan jihar Kano kuma dan takarar gwamna na jam’iyyar APC Dr. Nasiru Yusuf Gawuna ya yi alkawarin baiwa kananan hukumomin jihar ‘yancin cin gashin kansu idan aka zabe shi a matsayin gwamnan Kano .
Ya bayyana haka ne a lokacin da yake gabatar da wanj shiri na gidan talabijin din NTA Mai suna “The Balot”.
“Ƙananan Hukumomi wani bangare ne na gwamnati wanda yafi kusa da jama’a wanda ke taimakawa wajen cigaban al’umma ta kowacce fuska”. Inji Gawuna
“A matsayina na tsohon shugaban karamar hukumar na san abin da ya shafi gudanar da mulkinta”.
Lokacin da nake shugaban karamar hukuma, an ba ni damar yi aiki na yadda ya kamata, Hakan ta sa muka samu nasarori da dama don haka idan aka zabe mi a matsayin Gwamna nima zan basu damar cin gashin kansu”. Gawuna ya jaddada”.
Ya kara da cewa shi ne wanda ya fi cancanta kuma a shirye ya ke ya zama Gwamnan Jihar Kano bayan ya yi aiki da gwamnatocin da suka gabata kuma ya samu kwarewa da dama, duk da haka ya ba da tabbacin zai dora kan aiyukan da suka samu nasara akai kuma na kaucewa kura-kuran da sukai.
A sanarwar da babban Sakataren yada labaran mataimakin gwamna Hassan Musa Fagge ya aikowa kadaura24, yace Gawuna ya kuma bukaci al’umma musamman Matasa da su guji tada yayin zabe da bayan zabe don inganta zaman lafiyar da ake da su a kano.