Sarkin Kano ya taya zababben Shugaban kasa Bola Tinubu Murnar lashe zabe

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

Mai martaba Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero ya taya zababben Shugaban kasa Asiwaju Bola Ahmad Tinubu murnar lashe zaben Shugaban kasa da aka gudanar ranar Asabar 25 ga watan daya gabata.

Alhaji Aminu Ado Bayero ya bayyana hakan ne cikin wata wasika da ya aikawa Zababben Shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu.

Cikin wata sanarwa da babban Sakataren yada labarai na Masarautar Kano Abubakar Balarabe Kofar Na’isa ya aikowa kadaura24 a yammacin wannan rana ta talata.

Sanarwa tace Sarkin Kanon ya bayyana Bola Tinubu a matsayin Mai hangen nesa , duba da yadda ya ciyar da jihar legas gaba a lokacin da ya yi gwamnan jihar.

” Muna fatan zaka yi amfani da kwarewar da kake da ita iya Shugabanci wajen magance matsalolin da Nigeria take fuskanta a matsayin ka na Mai kishin al’umma da kasa baki daya”. Inji Sarkin Kano

Alhaji Aminu Ado Bayero ya kuma bada tabbacin zasu cigaba da yiwa zababben Shugaban kasar don ya sami nasara mulkar Nigeria cikin nasara.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...