Sarkin Kano ya taya zababben Shugaban kasa Bola Tinubu Murnar lashe zabe

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

Mai martaba Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero ya taya zababben Shugaban kasa Asiwaju Bola Ahmad Tinubu murnar lashe zaben Shugaban kasa da aka gudanar ranar Asabar 25 ga watan daya gabata.

Alhaji Aminu Ado Bayero ya bayyana hakan ne cikin wata wasika da ya aikawa Zababben Shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu.

Cikin wata sanarwa da babban Sakataren yada labarai na Masarautar Kano Abubakar Balarabe Kofar Na’isa ya aikowa kadaura24 a yammacin wannan rana ta talata.

Sanarwa tace Sarkin Kanon ya bayyana Bola Tinubu a matsayin Mai hangen nesa , duba da yadda ya ciyar da jihar legas gaba a lokacin da ya yi gwamnan jihar.

” Muna fatan zaka yi amfani da kwarewar da kake da ita iya Shugabanci wajen magance matsalolin da Nigeria take fuskanta a matsayin ka na Mai kishin al’umma da kasa baki daya”. Inji Sarkin Kano

Alhaji Aminu Ado Bayero ya kuma bada tabbacin zasu cigaba da yiwa zababben Shugaban kasar don ya sami nasara mulkar Nigeria cikin nasara.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...