Da dumi-dumi: Kotu ta aike da Alhassan Ado Doguwa gidan yari

Date:

Daga Isa Ahmad Getso

 

A ranar Laraba ne wata kotun majistare da ke Kano ta tasa keyar shugaban masu rinjaye na majalisar wakilai ta kasa Alhassan Ado Doguwa zuwa gidan yari har zuwa lokacin da ake neman belinsa.

 Wanda ake tuhuma, Alhassan Doguwa yana fuskantar shari’a ne akan laifuffuka da dama da suka hada da, zargin hada baki, kisan kai, mallakar bindiga ba bisa ka’ida ba, ta da hankalin al’umma da dai sauran su.
 Babban Alkalin Kotun, Ibrahim Mansur Yola ya bayar da umarnin a ci gaba da tsare wanda ake kara har zuwa ranar 7 ga Maris, 2023 don sauraron bukatar neman belin.
Idan za’a iya tunawa kadaura24 ta rawaito cewa jami’an tsaro sun kama Alhassan Ado Doguwa a filin jirgin sama na Malam Aminu kano akan hanyar sa ta tafiya kasar saudiyya domin gudanar da ibadar umarah .

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...