Ba za mu ɗauki malaman jami’ar da suke da ra’ayin siyasa aiki ba – INEC

Date:

Hukumar zaben Najeriya (INEC) ta ce ba za ta tura duk wani malamin jami’a da ke da alaka da wata siyasa aiki a zabukan kasar da za a fara nan da ‘yan kwanaki ba.

Sannan ta ce duk wani malamin jami’a da zai yi mata aikin wucin-gadi a zabukan kasar da ke tafe dole ne ya yi rantsuwar ‘yan ba-ruwanmu, wato ba ya wata jam’iyya ko siyasa ko goyon bayan wani dan takara.

Talla

Shugaban hukumar, Farfesa Mahmood Yakubu, ne ya sanar da haka jiya Alhamis a Abuja a lokacin wani taro da shugabannin jami’o’in kasar a Hukumar Jami’o’in Kasar (NUC).

Talla daukar nauyi Suraj Umar Wudil

Sai dai ya ce daman ita rantsuwar ta tabbatar da cewa mutum ba shi da wata jam’iyya ko dan siyasa ko takara da yake goyon baya, tana hawa kan dukkanin ma’aikatan zabe ne kamar yadda sashe na 26 na dokar zabe ta 2022 ya tanada.

Jaridar daily Trust ta ruwaito cewa, shugaban ya ce hukumar ba za ta tura duk wani malamin jami’a da ta san yana da alaka da wata jam’iyya ba.

“Haka suma wadanda watakila ba su shiga siyasa amma an san suna da dangantaka da wata siyasa ba za a dauke su ba. Hka suma wadnda aka yanke musu hukunci kan magudin zabe dole ne a ware su,” in ji shugaban na INEC.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...