Girgizar kasa: An ceto jaririya sabuwar haihuwa daga baraguzan gini

Date:

Masu aikin agaji sun ceto wata jaririya sabuwar haihuwa daga cikin baraguzan gine-ginen da suka rushe a sakamakon girgizar kasa a yankin arewa maso yammacin Syria ranar Litinin.

mahaifiyarta ta fara nakuda ne jim kadan bayan girgizar kasar, sannan ta haihu kafin ta rasu, in ji wani danginsu.
Majiyar ta ce mahaifin yarinyar da ‘yan uwanta hudu da kuma kanwar mahaifiyarta duk sun rasu a girgizar kasar.
An wani hoton bidiyo mai cike da mamaki an ga wani mutum na rike da jaririyar wadda ta yi budu-budu da kura, bayan da aka fito da ita daga cikin buraguzai a garin Jindayris.
Wani likita a wani asibiti na kusa da garin da aka ceto ta, Afrin ya ce jaririyar a yanzu tana nan cikin kyakkyawan yanayi.
Gidan da mahaifanta suke na daya daga cikin gine-gine 50 da rahotanni suka ce girgizar kasar mai karfin maki 7.8 ta lalata a Jindayris, wanda gari ne da ke hannun ‘yan hamayya a lardin Idlib da ke kusa da iyaka da Turkiyya.
Talla
Kawun jaririyar, Khalil al-Suwadi, ya ce suna samun labarin rugujewar ginin sai suka ruga domin su ga abin da ya faru.
”Mun ji murya a lokacin da muke tona buraguzai, ” kamar yadda ya sheda wa kamfanin dillancin labarai na AFP a ranar Talata.
Talla daukar nauyi Suraj Umar Wudil
”Da muka kawar da kasar sai muka samu jaririyar da mabiyiyarta, sai muka yanke mabiyiyar aka tafi da jaririyar asibiti.”
Likitan yara Hani Maarouf ya ce an kai jaririyar asibitinsa a yanayi maras kyau, saboda ta kukkuje ga kuma tsananin sanyi da ya taba ta”.
”To amma yanzu ta samu sauki,” in ji likitan.
An gudanar da jana’iza ta gaba-daya ga mahaifiyarta Afraa, da mahaifinta Abdullah da kuma ‘yan uwanta hudu.
Suna daga cikin mutane 1,800 da aka san cewa sun rasu a girgizar kasar a Syria, kamar yadda bayanai suka nuna.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...