‘Yan sandan Ghana sun haramta hasashen abubuwan da za su faru a sabuwar shekara

Date:

Yan sandan Ghana sun gargaɗi shugabannin addinai game da al’adar hasashen abubuwan da za su faru a sabuwar shekara, wanda ke janyo fargaba da rikici har ma da mace-mace a ƙasar.

 

A wata sanarwa da ‘yan sandan ƙasar ta fitar ta ce bai kamata ‘yancin addini ya saɓa wa ‘yancin wasu ba.

 

Masu suka dai na ganin wannan sabuwar doka a matsayin wacce ta saɓa wa ‘yancin addini wanda kundin tsarin mulkin ƙasar ya tanadar, dan haka dokar ba ta kan ƙa’ida.

Talla

Miliyoyin kiristoci ne dai ke taruwa a majami’u domin sauraron hasashen abubuwan da za su faru a shekara mai kamawa daga bakunan fastocinsu.

 

Sakonnin kan kunshi bushara kan abubuwa na farin ciki da garɗari kan munanan abubuwa.

 

‘Yan sandan sun sanya wannan doka ne bayan a shekarar da ta gabata aka yi hasashen samun yawan mace-mace da bala’o’i masu yawa a ƙasar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...