‘Yan sandan Ghana sun haramta hasashen abubuwan da za su faru a sabuwar shekara

Date:

Yan sandan Ghana sun gargaɗi shugabannin addinai game da al’adar hasashen abubuwan da za su faru a sabuwar shekara, wanda ke janyo fargaba da rikici har ma da mace-mace a ƙasar.

 

A wata sanarwa da ‘yan sandan ƙasar ta fitar ta ce bai kamata ‘yancin addini ya saɓa wa ‘yancin wasu ba.

 

Masu suka dai na ganin wannan sabuwar doka a matsayin wacce ta saɓa wa ‘yancin addini wanda kundin tsarin mulkin ƙasar ya tanadar, dan haka dokar ba ta kan ƙa’ida.

Talla

Miliyoyin kiristoci ne dai ke taruwa a majami’u domin sauraron hasashen abubuwan da za su faru a shekara mai kamawa daga bakunan fastocinsu.

 

Sakonnin kan kunshi bushara kan abubuwa na farin ciki da garɗari kan munanan abubuwa.

 

‘Yan sandan sun sanya wannan doka ne bayan a shekarar da ta gabata aka yi hasashen samun yawan mace-mace da bala’o’i masu yawa a ƙasar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...