Daga Khadija Abdullahi Aliyu
Dan takarar mataimakin Shugaban Kasa na Jam’iyyar APC Sanata Kashim Shattima yace Idan Akai la’akari da tarin arzikin kasa da ake da shi a Arewacin Nigeria bai kamata a sami talauci a yankin ba.
Sanata Kashim Shattima ya bayyana hakan ne lokacin da ya ziyarci gidan tsohon gwamnan jihar Kaduna zamanin mulkin soja Gen. Lawan Jafaru Isa Mai ritaya .

- ” Mun je jihar jigawa jiya mun ga arzikin kasa haka a nan kano ma, ta yadda ko takardar kudi aka shuka sai ta tsiro saboda yadda Allah ya albarkaci mu da albarkar kasa da kuma yawan jama’a , don haka babu dalilin da za’a Sami talauci a Arewacin Nigeria”. Inji Shattima
Yace akwai yiwuwar nan da shekara ta 2050 Nigeria zata zama ta uku cikin jerin kasashen da suka fi yawan al’umma a duniya Inda zai zama daga Chana sai Indian sai Kuma Nigeria.
Kashim Shattima ya kara da cewa a shekara ta 2050 arewacin Nigeria zai kasance da kaso 70 na yawan al’ummar Nigeria, don haka ya bukaci shugabannin arewa su gada kai don samarwa yankin makoma Mai kyau.
A shirye muke mu taimaka don inganta aiyukan yan Hisbah a Kaduna – Kwamandan Hisbah na Kano
Ya yi alkawarin idan suka lashe zaben 2023, gwamnatin su zata bujiro da hanyoyin da zasu samar wa matasa aiyukan yi don inganta Rayuwar su da tattalin arzikin kasa.
Da yake nasa jawabin Gen. Lawan Jafaru Isa ya bada tabbacin zai cigaba da yin duk mai yiyuwa wajen ganin jam’iyyar APC ta yi nasara a dukkanin zabukan dake tafe ta karkashin kungiyar sa .
Kashim Shattima ya kuma ziyarci Alhaji Musa Gwadabe wanda ya je ya duba shi tare da neman tabarrakinsa a takarar da suke yi kasancewar sa cikin iyayen jam’iyyar APC na kasa.