Ba zamu lamunci ayi amfani da gwamnatin tarayya don yi mana magudi ba – Gwamnan Bauchi

Date:

 

 

Gwamnan Jihar Bauchi Bala Mohammed ya yi zargin cewa ana yunkurin yi masa magudi a zaben gwamnan da za a gudanar a 2023.

 

Ya bayyana haka ne ranar Lahadi a gidan gwamnatin jihar Bauchi yayin da kungiyar Kiristoci ta jihar ta kai masa ziyarar bikin Kirsimeti.

Talla

Gidan talbijin na Channels TV ya ambato Gwamna Bala Mohammed yana cewa mutanen da suke yunkurin yin amfani da karfin gwamnatin tarayya domin yin magudin zabe ba za su yi nasara ba domin Shugaba Muhammadu Buhari ba zai bari hakarsu ta cimma ruwa ba.

 

“Akwai mutanen da ke sayen kuri’u, da kuma wadanda suke shirin murde zabe ta hanyar amfani da karfin gwamnatin tarayya amma na sani cewa Shugaba Buhari mutum ne mai adalci, kuma tuni ya tabbatar mana cewa zai bar mutane su zabi wanda suke so,” in ji shi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...