Ba zamu lamunci ayi amfani da gwamnatin tarayya don yi mana magudi ba – Gwamnan Bauchi

Date:

 

 

Gwamnan Jihar Bauchi Bala Mohammed ya yi zargin cewa ana yunkurin yi masa magudi a zaben gwamnan da za a gudanar a 2023.

 

Ya bayyana haka ne ranar Lahadi a gidan gwamnatin jihar Bauchi yayin da kungiyar Kiristoci ta jihar ta kai masa ziyarar bikin Kirsimeti.

Talla

Gidan talbijin na Channels TV ya ambato Gwamna Bala Mohammed yana cewa mutanen da suke yunkurin yin amfani da karfin gwamnatin tarayya domin yin magudin zabe ba za su yi nasara ba domin Shugaba Muhammadu Buhari ba zai bari hakarsu ta cimma ruwa ba.

 

“Akwai mutanen da ke sayen kuri’u, da kuma wadanda suke shirin murde zabe ta hanyar amfani da karfin gwamnatin tarayya amma na sani cewa Shugaba Buhari mutum ne mai adalci, kuma tuni ya tabbatar mana cewa zai bar mutane su zabi wanda suke so,” in ji shi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...