Wasu sun so tada hankali a Nigeria amma sun gaza – Buhari

Date:

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya ce masu son tayar da fitina a ƙasar “sun gaza yin hakan”, yana mai cewa “alkairi na tafe a 2023 da gabanta” cikin jawabin Kirsimetinsa na ƙarshe a matsayin shugaban ƙasa.

 

Cikin jawabin da ya gabatar a ranar Asabar, Buhari ya jaddada cewa nan da watan Mayu gwamnatinsa za ta miƙa mulki ga sabuwar gwamnatin da za a zaɓa a babban zaɓe na watan Fabarairu.

 

Talla

“Saƙona kenan na Ranar Kirsimeti a matsayin shugaban ƙasa,” in ji shi. “Nan da mako 22 daga yanzu wannan gwamnatin za ta miƙa mulki ga wata.”

 

 

Kazalika, ya bayyana miƙa mulkin a matsayin “dama ta tabbatar da kafuwar dimokuraɗiyya a Najeriya kamar yadda ƙasashen waje suka sani”.

 

A cewarsa: “Mu ci gaba da zama lafiya cikin annashuwa har zuwa sabuwar shekara da kuma lokacin zaɓe a watan Fabarairu da ma gaba.

 

“Ina tabbatar wa ‘yan Najeriya cewa waɗanda ke neman tayar da fitina a ƙasarmu sun gaza a yunƙurinsu.”

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...