Wasu sun so tada hankali a Nigeria amma sun gaza – Buhari

Date:

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya ce masu son tayar da fitina a ƙasar “sun gaza yin hakan”, yana mai cewa “alkairi na tafe a 2023 da gabanta” cikin jawabin Kirsimetinsa na ƙarshe a matsayin shugaban ƙasa.

 

Cikin jawabin da ya gabatar a ranar Asabar, Buhari ya jaddada cewa nan da watan Mayu gwamnatinsa za ta miƙa mulki ga sabuwar gwamnatin da za a zaɓa a babban zaɓe na watan Fabarairu.

 

Talla

“Saƙona kenan na Ranar Kirsimeti a matsayin shugaban ƙasa,” in ji shi. “Nan da mako 22 daga yanzu wannan gwamnatin za ta miƙa mulki ga wata.”

 

 

Kazalika, ya bayyana miƙa mulkin a matsayin “dama ta tabbatar da kafuwar dimokuraɗiyya a Najeriya kamar yadda ƙasashen waje suka sani”.

 

A cewarsa: “Mu ci gaba da zama lafiya cikin annashuwa har zuwa sabuwar shekara da kuma lokacin zaɓe a watan Fabarairu da ma gaba.

 

“Ina tabbatar wa ‘yan Najeriya cewa waɗanda ke neman tayar da fitina a ƙasarmu sun gaza a yunƙurinsu.”

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...