Yanzu-Yanzu: Shekarau ya Magantu kan hukuncin kotun da ya tabbatar da Muhd Abacha a takarar gwamnan kano na PDP

Date:

Daga Aisha Aliyu Umar

Tsohon gwamnan Kano kuma jagoran jam’iyyar adawa ta PDP a jihar, Ibrahim Shekarau, ya ce suna jiran umarnin da uwar jam’iyyarsu ta ƙasa za ta bayar bayan kotu ta bai wa Mohammed Abacha takarar gwamnan Kanon.

Shekarau ya faɗa wa BBC Hausa cewa “burinmu shi ne ‘yan jam’iyya su natsu, ɓangaren da ya yi nasara da wanda bai yi ba su kwantar da hankalinsu har sai an samu umarni daga jam’iyya”.

A ranar Alhamis ne Babbar Kotun Tarayya da ke Kano ta tabbatar da Mohammed Abacha a matsayin halastaccen ɗan takarar gwamna a PDP tare da soke zaɓen fitar da gwanin da ya bai wa Sadiq Aminu Wali nasara.

Talla

Hakan na nufin ɓangaren shugabancin Shehu Wada Sagagi ne ya yi nasara, wanda ya shirya zaɓen, saɓanin ɓangaren Sanata Bello Hayatu Gwarzo da ke mara wa Sadik Wali baya.

Shekarau ya shiga PDP a watan Augusta bayan rashin jituwa tsakaninsa da jagora kuma ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NNPP, Rabiu Kwankwaso.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...