Yanzu-Yanzu: Shekarau ya Magantu kan hukuncin kotun da ya tabbatar da Muhd Abacha a takarar gwamnan kano na PDP

Date:

Daga Aisha Aliyu Umar

Tsohon gwamnan Kano kuma jagoran jam’iyyar adawa ta PDP a jihar, Ibrahim Shekarau, ya ce suna jiran umarnin da uwar jam’iyyarsu ta ƙasa za ta bayar bayan kotu ta bai wa Mohammed Abacha takarar gwamnan Kanon.

Shekarau ya faɗa wa BBC Hausa cewa “burinmu shi ne ‘yan jam’iyya su natsu, ɓangaren da ya yi nasara da wanda bai yi ba su kwantar da hankalinsu har sai an samu umarni daga jam’iyya”.

A ranar Alhamis ne Babbar Kotun Tarayya da ke Kano ta tabbatar da Mohammed Abacha a matsayin halastaccen ɗan takarar gwamna a PDP tare da soke zaɓen fitar da gwanin da ya bai wa Sadiq Aminu Wali nasara.

Talla

Hakan na nufin ɓangaren shugabancin Shehu Wada Sagagi ne ya yi nasara, wanda ya shirya zaɓen, saɓanin ɓangaren Sanata Bello Hayatu Gwarzo da ke mara wa Sadik Wali baya.

Shekarau ya shiga PDP a watan Augusta bayan rashin jituwa tsakaninsa da jagora kuma ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NNPP, Rabiu Kwankwaso.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...