Gwamnatin tarayya ta bayyana ranakun hutun kirsimeti da sabuwar shekara

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Gwamnatin tarayya ta ayyana ranakun 26 da 27 ga watan Disamba da kuma 2 ga watan Janairun 2023 a matsayin ranakun hutu domin gudanar da bukukuwan Kirsimeti da na sabuwar shekara.

 

Ministan cikin gida Alhaji Rauf Aregbesola ne ya tabbatar da hakan a wata sanarwa mai dauke da sa hannun babban sakataren ma’aikatar Belgore Shuaib a ranar Juma’a.

Talla

 

Sanarwar ta kara da cewa, bukukuwan su ne na bikin Kirsimeti, da washegarin ranar, da bikin Sabuwar Shekara .

 

Aregbesola ya umurci Kiristoci da su yi koyi da Yesu kuma su yi tunani a kan koyarwarsa yayin da suke bikin.

 

 

Ya kuma yi kira ga mabiya addinin kirista da kada su bari masu ra’ayin aikata laifuka su ingiza su su haifar da rikici a kasar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...