Gwamnatin tarayya ta bayyana ranakun hutun kirsimeti da sabuwar shekara

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Gwamnatin tarayya ta ayyana ranakun 26 da 27 ga watan Disamba da kuma 2 ga watan Janairun 2023 a matsayin ranakun hutu domin gudanar da bukukuwan Kirsimeti da na sabuwar shekara.

 

Ministan cikin gida Alhaji Rauf Aregbesola ne ya tabbatar da hakan a wata sanarwa mai dauke da sa hannun babban sakataren ma’aikatar Belgore Shuaib a ranar Juma’a.

Talla

 

Sanarwar ta kara da cewa, bukukuwan su ne na bikin Kirsimeti, da washegarin ranar, da bikin Sabuwar Shekara .

 

Aregbesola ya umurci Kiristoci da su yi koyi da Yesu kuma su yi tunani a kan koyarwarsa yayin da suke bikin.

 

 

Ya kuma yi kira ga mabiya addinin kirista da kada su bari masu ra’ayin aikata laifuka su ingiza su su haifar da rikici a kasar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Abubakar Bichi ya bada gudumawar motocin bas 13 ga jami’o’in Kano da taraktoci 11 ga yan mazabarsa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu Dan Majalisar tarayya mai wakiltar karamar...

Rikicin Sarautar Kano: Fadar Sarki Sanusi ta zargi magoya bayan Sarki Aminu Ado Bayero da kai farmaki Kofar Kudu

Daga Sani Idris Maiwaya   Rikicin Masarautar kano ya na neman...

Shugabannin Kasuwar Kanti Kwari sun shiryawa Gwamnan Kano Addu’o’i na musamman

Daga jafar adam Shugaban kasuwar Kantin Kwari Sharu Abdullahi Namalam...