A shirye nake na sanya hannu don zartar da hukuncin rataye Abduljabbar —Ganduje

Date:

Daga Maryam Ibrahim zawaciki

Gwamnatin jihar Kano ta ce gwamna Abdullahi Umar Ganduje a shirye ya ke ya sanya hannu kan sammacin kashe malamin addinin Musuluncin nan, Sheikh Abduljabbar Nasiru Kabara.

 

Kwamishinan shari’a kuma babban lauyan jihar, Lawan Musa ne ya bayyana hakan a lokacin da yake mayar da martani kan hukuncin da aka yankewa Abduljabbar na hukuncin kisa ta hanyar rataya, bayan da wata kotun shari’ar musulunci ta same shi da laifin yin kalaman batanci ga Annabi S A W .

 

Musa ya ce gwamnan a shirye yake domin ganin ba a karya doka da oda a jihar kano ba, inda ya ce hukuncin da kotun ta yanke akan malamin gwamnatin jihar ta shigar da karar malamin, wanda hakan ke nuna babu wanda fi karfin doka.

Talla

“Ba za a bar kowa ya karya doka ba tare da daukar matakan da suka dace akansa ba.

“Mun kai shi (Abduljabbar) kotu, muka ba shi dukkan abubuwan da ya kamata domin ya kare kansa, kuma a yau mun gode wa Allah, kotu ta gamsu da hujjojin da muka gabatar a kansa, kuma ta yanke masa hukuncin da ya dace,” inji shi.

 

Musa ya kara da cewa: “Kamar yadda gwamna bai canza matsayarsa ba a al’amarin Hanifa, haka nan ma ba ta canza ba akan wannan lamari.

 

“Kun san akwai tsare-tsare da yawa da ya kamata a bi kuma mai girma Gwamna a shirye yake; da zarar an kawo masa wannan takardar, zai sa hannu domin zartar da hukuncin”. a cewar kwamishinan

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...