Hajj 2022: NAHCON ta Gaza sauke nauyin da aka dora mata – Ganduje

Date:

Gwamnatin jihar kano ta bukaci gwamnatin tarayya data bincika tare da hukunta shugabannin kula da aikin hajji ta kasa Nahcon sakamakon gazawarsu wajen shirya aikin hajji bana yadda ya kamata.

 

Gwamnan jihar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje ne ya bayyana hakan lokacin da yake karbar rahoton aikin hajjin bana daga hukumar Jin dadin alhazai ta jihar kano.

Talla

Gwamna Ganduje yace tun da ya zama gwamnan kano bai taba ganin yadda hukumar tayi Rashin tsari ba kamar shekarar data wuce, Inda yace akwai rashin gaskiya da kwarewa a aiyukan shugabannin hukumar Nahcon na wannan karo.

 

” Sun cuci alhazai su cuci ma’aikata, sun kawo chanje-chanje marasa ma’ana, sun kawo Rashin gaskiya da son rai sun kasa kai alhazai Kuma sun cucesu”. Inji Ganduje

” Sun bamu jirgin da zai yi jigilar alhazan mu, mun fada musu bama so, ni da katina ma sai da naje har ofishin hukumar dake abuja na Kuma koka musu suka ce min zasu gyara, Amma bayan tahowa ta suka ki chanzawa”.

 

Ganduje ya kuma bukaci gwamnatin tarayya da majalisar wakilai ta kasa da su bincika domin daukar matakan da suka dace don hana faruwar hakan a nan gaba.

 

Ya kuma yabawa hukumar Jin dadin alhazai ta jihar kano bisa yadda suka gudanar da kyakyawan tsari a aikin hajjin daya gaba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...