Hajj 2022: NAHCON ta Gaza sauke nauyin da aka dora mata – Ganduje

Date:

Gwamnatin jihar kano ta bukaci gwamnatin tarayya data bincika tare da hukunta shugabannin kula da aikin hajji ta kasa Nahcon sakamakon gazawarsu wajen shirya aikin hajji bana yadda ya kamata.

 

Gwamnan jihar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje ne ya bayyana hakan lokacin da yake karbar rahoton aikin hajjin bana daga hukumar Jin dadin alhazai ta jihar kano.

Talla

Gwamna Ganduje yace tun da ya zama gwamnan kano bai taba ganin yadda hukumar tayi Rashin tsari ba kamar shekarar data wuce, Inda yace akwai rashin gaskiya da kwarewa a aiyukan shugabannin hukumar Nahcon na wannan karo.

 

” Sun cuci alhazai su cuci ma’aikata, sun kawo chanje-chanje marasa ma’ana, sun kawo Rashin gaskiya da son rai sun kasa kai alhazai Kuma sun cucesu”. Inji Ganduje

” Sun bamu jirgin da zai yi jigilar alhazan mu, mun fada musu bama so, ni da katina ma sai da naje har ofishin hukumar dake abuja na Kuma koka musu suka ce min zasu gyara, Amma bayan tahowa ta suka ki chanzawa”.

 

Ganduje ya kuma bukaci gwamnatin tarayya da majalisar wakilai ta kasa da su bincika domin daukar matakan da suka dace don hana faruwar hakan a nan gaba.

 

Ya kuma yabawa hukumar Jin dadin alhazai ta jihar kano bisa yadda suka gudanar da kyakyawan tsari a aikin hajjin daya gaba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...