Bayan rusa kan ta jam’iyyar PRP ta haɗe da APC a Sakkwato

Date:

Daga Aliyu Nasir Zangon Aya

 

Yayin da ‘yan watanni ya rage a gudanar da zabukan 2023, daukacin jam’iyyar PDP ta Jihar Sakkwato ya ruguje ta haɗe da jam’iyyar APC a jihar.

 

 

Dukkanin matakan jam’iyyar, karkashin dan takararta na gwamna, Sa’idu Muhammad Gumburawa ya narke zuwa jam’iyyar APC.

Talla

 

Wadanda suka sauya sheka sun hada da daukacin ‘yan takarar sanatoci uku na PRP a, da daukacin ‘yan majalisar wakilai, da ‘yan takarar majalisar jiha, da kuma dukkan jami’an jam’iyyar daga jiha zuwa kananan hukumomi.

An sace kayan fitar angwanci na wani ango a Kano

 

Jagoran jam’iyyar, wanda kuma shine mai rike da tutar gwamna a jihar, Sa’idu Muhammad Gumburawa, ya sanar da jagoran jam’iyyar APC, Sanata Aliyu Wamakko cewa sun yanke shawarar ficewa daga tsohuwar jam’iyyarsu ne domin bayar da gudunmawarsu wajen ganin nasarar APC a 2023 a jihar.

Wata babbar mota ta hallaka jami’an Road Safety 2

 

Ya kuma bayyana cewa duba da halin da al’ummar jihar suka tsinci kansu a karkashin gwamnatin PDP, sun shiga APC ne domin hada kai da shugabanninta sannan kuma su ci zabe a dukkanin matakai domin jihar ta dawo kan martabarta kamar yadda take a zamanin gwamnatin tsohon gwamna Aliyu Wamakko.

 

 

Da ya ke jawabi a lokacin da yake karbar wadanda suka sauya sheka zuwa APC, Wamakko ya bayyana Gumburawa a matsayin aboki kuma abokin hadin gwiwa na gari.

 

 

Ya bayyana farin cikinsa da zuwansa APC tare da bayyana APC a matsayin jam’iyyar duk mai son ci gaban jihar Sakkwato.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...