Wata babbar mota ta hallaka jami’an Road Safety 2

Date:

Daga Auwal Alhassan Kademi

 

Wani direban babbar mota ya kashe jami’an Hukumar Kiyaye Aukuwar Hadura ta Najeriya biyu a kan babbar hanyar Aba da ke kudancin ƙasar.

 

A wata sanarwa da hukumar ta fitar mai ɗauke da sannun babban jami’in wayar da kan jama’a na hukumar Bisi Kazeem, ya ce muƙaddashin babban shugaban Hukumar Dauda Ali Biu, ya bayyana damuwarsa game da kashe jami’an hukumar biyu, tare da alkawarta gurfanar da waɗanda suka yi sanadiyyar mutuwar jami’an a gaban kotu domin su fuskanci hukunci .

 

Talla

Sanarwa ta ce Mista Biu ya yi Allah wadai da wannan lamari da ya yi sanadiyyar mutuwar jami’an hukumar waɗanda ke bakin aikinsu, sakamakon abin da ya kira ‘aikin direbobi masu tukin ganganci waɗanda ke ci gaba da karya dokar tuƙi’

An sace kayan fitar angwanci na wani ango a Kano

Lamarin ya faru ne sakamakon ƙoƙarin kauce wa rami da direban babbar motar ya yi, yayin da yake tsaka da gudu a kan hanyar, kamar yadda sanarwar ta bayyana.

 

Jami’an hukumar FRSC dai sun daɗe suna zargin direbobin ƙasar da tukin ganganci tare da gudun wuce kima a kan titunan ƙasar, lamarin da hukumar ke cewa shi ne musabbabin mafi yawancin haduran da ke aukuwa a kan titunan ƙasar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...