Mun gamsu da kulawar da Gwamnatin Ganduje take baiwa Ilimin addini da na Zamani – Sarkin Kano

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

Mai Martaba Sarkin Kano Alh Aminu Ado Bayero CFR ya yabawa Gwamnatin Dr. Abdullahi umar Ganduje bisa kulawar da take baiwa Ilimin addinin Musulunci da na Zamani a jihar.

 

 Mai martaba Sarkin ya yi wannan yabon ne a wajen bikin yaye dalibai tamanin da daya na makarantar Ulumul quar,an li imamu Dalhatu, Islamiyya Soron Danki a karamar hukumar birni.
 Alh. Aminu Ado Bayero, ya taya daliban murna tare da bukatar su da su yi amfani da ilimin da suka samu tare da yaba wa kokarin malaman makarantar wajen inganta tarbiyyar daliban.
 Sarkin wanda ya yi jawabi mai tsaho kan muhimmancin Ilimi, ya kuma bayyana ilimin kur’ani a matsayin ginshikin duk wani ilimi a rayuwar dan Adam.
Talla
Cikin sanarwar da sakataren yada labaran Masarautar kano Abubakar Balarabe Kofar Na’isa ya aikowa kadaura24, yace Alhaji Aminu Bayero, ya yi kira ga Masu dukiyoyi a cikin al’umma da su rika tallafa wa karatun kur’ani a tsakanin daliban da suka kammala karatu domin bunkasa ilimin kur’anin da suka samu.
 Da yake jawabi a wajen taron shugaban makarantar Malam Habibu Abbas ya bayana tarihin makarantar da cewa an kafa makarantar tun shekarar 2010 da dalibai ashirin da takwas, kuma a yanzu haka tana da dalibai sama da dari da hamsin da shida da malamai da dama.
 A nata bangaren, Malama Tasalla Nabulusi Bako, ta shawarci jama’a da su rika cika alkawuran da suka dauka a kowane lokaci, ta kuma yaba wa mai martaba Sarkin Musulmi Aminu Bayero bisa kulawar da yake baiwa cigaban Ilimi don bunkasa shi

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...