Buhari ya amince da sake fasalin Naira, CBN ta mayar da martani ga Ministan Kudi

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu
 Babban bankin Najeriya (CBN) ya ce ya bi ka’idojin da suka dace wajen sake fasalin wasu nau’ukan Naira guda uku.
Jami’in hulda da jami’a na babban bankin, Mista Osita Nwanisobi ne ya bayyana haka a lokacin da yake mayar da martani ga ministar kudi, kasafin kudi da tsare-tsare ta kasa, Zainab Ahmed, wadda ta ce ba’a sanar da ma’aikatar ta ba.
Kadaura24 ta rawaito Nwanisobi ya bayyana mamakinsa da ikirarin na ministan, yana mai jaddada cewa CBN ya komai nasa bisa doka da oda.
Talla
Ya ce hukumar gudanarwar ta CBN bisa tanadin sashe na 2 (b) da sashe na 18 (a) da sashe na 19 (a) (b) na dokar CBN ta shekarar 2007, sun nemi amincewar shugaban kasa Muhammadu a rubuce Kuma Buhari ya amince da sake fasalin kuma takardun kudi na N200, N500, da N1,000.
Ya yi kira ga ‘yan Najeriya da su marawa aikin sake fasalin kudin kasar baya, inda ya ce hakan yana da amfani ga ‘yan Najeriya baki daya, yana mai kara jaddada cewa wasu mutane na tara makudan kudade a gidaje Maimakon a bankuna .
Wannan al’amari, a cewarsa, bai kamata duk wanda ke nufin alheri ga kasa ya kalubalence shi ba.
Don haka Nwanisobi ya bukaci ‘yan Najeriya, ba tare da la’akari da matsayinsu ba, da su goyi bayan aikin sake fasalin Naira, domin yana da amfani ga tattalin arzikin kasa

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...