Falakin Shinkafi ya bada gudunmawar kayan kwallo ga F/c Yakasai

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

A kokarin sa Kara sada zumunci da Kuma zaburar da matasa Falakin Shinkafi Kuma Jarman matasan Arewa Amb. Dr. Yunusa Yusuf Hamza ya bada gudunmawar kayan kwallo domin su ji dadi yin wasanni.

 

Lokacin da ya ke mika kayan ga kungiyar kwallon kafa ta Super star Yakasai, Dr. Yunusa Yusuf ya yaba da yadda yan kungiyar suke gudanar da wasannin su cikin kwanciyar hankali da lumana.

Talla

 

” Na yi matukar gamsuwa da yadda kuke harkokin wasannin ku ba tare da fada da juna ba, hakan tasa naga dacewar na bada tawa gudunmawar don ku cigaba da sada zumunci da kuma motsa jiki yadda ya kamata”. Inji Jarman matasan Arewa

 

Dr. Yunusa Yusuf Hamza yace kamata yayi matasan wannan lokaci musamman masu harkar wasanni su rika zaman lafiya da juna musamman a lokacin wasa, saboda kwallon kafa tana sada zumunci sosai baya ga inganta lafiya da take yi.

 

” Ina fata wannan riguna da muka kawo muku zasu kara muku kwarin gwiwar cigaba da samun nasarar a wasannin da zaku buga a nan gaba, kuma zaku cigaba da ɗauko mana kofi a wasannin masu zuwa “. Inji Jarman matasan Arewa

Wasu daga cikin kayan da Falakin Shinkafi ya bayar

Shugaban kungiyar kwallon kafan ta Super star Yakasai wanda ya karbi kayan a madadin ‘ya’yan kungiyar ya yabawa Amb. Dr. Yunusa Yusuf bisa tallafin kayan da ya basu, sannan sun bada tabbacin zasu Kara kaimi wajen samun nasarar a wasannin da zasu buga a nan gaba.

 

Ya ce kayan zasu Kara musu kaimi wajen cigaba da sada zumuncin da aka basu kayan domin su.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...