IPMAN ta bayyana dalilin da yasa aka sami karancin man fetur

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Kungiyar dillalan man fetur mai zaman kanta ta Najeriya IPMAN, ta yi kira ga ‘yan Najeriya da su yi hakuri yayin da ake kokarin shawo kan matsalar karancin man da ake fama da shi a halin yanzu sakamakon ambaliyar ruwa da ta kai ga lalata wasu manyan tituna a wasu sassan jihohin Arewacin kasar nan.

Kadaura24 ta rawaito Shugaban kungiyar IPMAN reshen Arewacin Najeriya, Alhaji Bashir Danmalam ne ya yi wannan kiran a wata sanarwa da ya raba wa manema labarai a ranar Asabar.
 Shugaban IPMAN ya bayyana cewa ana sa ran motoci kusan 200 dake dauke da man fetur daga Calabar ana sa ran su isa Abuja da sauran sassan jihohin Arewa domin rabawa gidajen mai.
Talla
 Ya ce ana sa ran motocin za su bi ta Ikom, Ogoja, Katsina Ala, Vandeikia har zuwa Lafiya zuwa Abuja.
 Danmalam ya yabawa Manajan Daraktan Kamfanin (PPMC), Alhaji Isyaku Abdullahi bisa alkawarin tallafa wa ‘yan kasuwar da man dizal domin rage musu wahalhalun da suke fuskanta sakamakon tsadar dizal din .
 Ya ce kamfanin sarrrafa albarkatun mai na NNPC tare da hadin gwiwar IPMAN na kokarin ganin an samar da isassun mai da kuma rarraba shi, inda ya ce nan ba da dadewa ba za a kawo karshen karancin man fetur din .
 Ya kuma bayyana cewa, kamfanin na NNPC ya kuma tattara jami’an hukumar kiyaye haddura ta kasa domin su taimaka wajen kawar da tsinkoso a hanyoyin da abin ya shafa domin jigilar kayayyaki cikin sauki zuwa sassan Arewacin kasar nan.
 Bugu da kari, ya ce kamfanin na NNPC ya umurci kamfanin CCC na yan kasar China da ke aikin hanyoyin da abin ya shafa su koma wuraren da suka lalace domin su.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Majalisar Dokokin Kano ta yi Doka kan masu tufar da yawu da majina a titi

Majalisar Dokokin jihar Kano ta amince da dokar cin...

Sanata Barau zai baiwa dalibai 1,000 tallafin karatu a Kano ta tsakiya da ta Kudu

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau...

Kamfanin Gerawa ya ba da tallafin Kwamfutoci 100 ga al’ummar Gezawa

Daga Abdulmajid Habib Tukuntawa   Kamfanin shinkafa na Gerawa Rice Mills...

Gwamnan Kano ya baiwa maja-baƙin Sheikh Karibullah da wasu malamai muƙami

    Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf ya amince...