Daga Isa Ahmad Getso
Shahararren dan wasan barkwancin nan na masana’antar Kannywood Aminu Baba Ari yace mahassadansa ne suke kokarin sai sun zubar masa da kimar da yake da ita a cikin mutane, yasa suke cewa ya tattaka wata malamar Islamiyya.
Baba Ari ya bayyana hakan ne a wata ganawa ta musamman da yayi da Kadaura24 a Kano.
” Duk wanda ya zo yaga ‘yarsa a halin da na ga tawa ‘yar dole sai hankalinsa ya tashi, to Amma kuskuren da nayi shi ne nakai mata duka Kuma ban same ta ba sai na sami gefenta, Kuma na fahimci nayi kuskure na Kuma yi nadama har na baiwa malamar da iyayen ta da hukumar makarantar hakuri akan kuskuren da na yi”. Inji Baba Ari
Baba Ari yace bai kamata maganar ta yi nisan da ta yima Amma duk Abun da makiya suka shiga dole sai dai mutum yayi hakuri, Amma babu shakka an zalunceni da aka ce wai na yiwa malamar dukan tsiya har na tattakata Wannan magana sharrice Kuma na bar wadanda sukai min da mahaliccinmu”.
Yace duk wani dan unguwar Kofar Nasarawa yasan shi ba mafadaci bane Kuma baya cikin batagari a unguwar su ko masana’atar Kannywood , Amma ya fahimci akwai masu yi masa bita da kulli, Inda yace ya bar su da Allah.
Al’umma da dama dai sun yi mamakin yadda aka ce Aminu Baba Ari yayi wancen aikin ,Amma dai da Wannan bayani nasa watakila ya sauya yadda al’umma suka fahimci labarin.