Rashin kyawun hanya, yasa al’ummar wasu garuruwa a Gwarzo yin barazanar kin fitowa zaben 2023

Date:

Daga Aleeyu Abdullahi Danbala Gwarzo
Al’ummar garuruwan Rafawa da Dogami da Munawa da lahadin kara da dogami da tudunkudi da sauran kauyikan da suke kusa da yankin a karamar hukumar Gwarzo sun ce zasu kauracewa zaben shekara ta 2023 saboda rashi yi musu hanyar data hade garuruwansu.
Kadaura24 ta rawaito Shugaban kungiyar cigaban garuruwan Ahmad Musa Siri ne ya bayyana hakan yayin da suka gudanar da taron neman hadin kan al’umma yankin.
 “Matukar mahukunta ba su zo sunyi mana aikin hanyar nan ba kafin zabe to muna shida musu cewa kada ma a kawo mana akwatunan zabe domin babu Wanda zai fito don ya kada kuri’a zaben banana wannan ita ce matsayarmu” . A cewar Musa siri
Talla
Ya kara da cewa al’ummar dake yankin suna shan bakar wahala sosai wajen fitar da marasa lafiya zuwa asibiti, saboda saboda basu da asibiti a yankin sai sun fito cikin garin Gwarzo, a wani lokaci marasa lafiya kan rasa ryukansu kafin a karaso zuwa Gwarzo a dalilin lalacewar hanyar.
“Alhamdulillah mun sami goyon bayan dukkanin al’ummar mu Kuma muddin gwamnati bata zo ta gyara mana hanyar mu ba, to baza mu yi zaben shekara ta 2023 wannan ita ce matsayarmu.” Inji Musa Siri
Daga karshe Shugaban kungiyar yayi kira ga mahukunta dasu dubi halin da al’ummar su suke ciki ayi musu wannan hanyar ko dan a inganta Rayuwar su.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kamfanin Gerawa ya ba da tallafin Kwamfutoci 100 ga al’ummar Gezawa

Daga Abdulmajid Habib Tukuntawa   Kamfanin shinkafa na Gerawa Rice Mills...

Gwamnan Kano ya baiwa maja-baƙin Sheikh Karibullah da wasu malamai muƙami

    Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf ya amince...

Mamallakin jaridar Nigerian Tracker ya zama Ma’ajin kungiyar masu yada labarai a kafar yanar gizo ta Arewa

Kungiyar masu yada labarai a kafafen sadarwa na zamani...

Rusau: Ana zargin an harbi mutane 6 a unguwar Rimin zakara dake Kano

Daga Nazifi Dukawa   Mazauna Unguwar Rimin Zakara da ke Karamar...