Maulid: Koyi da halayen Annabi S A W ne zasu kawo mafita a halin da Nigeria take ciki – Atiku Abubakar

Date:

Daga Aisha Aliyu Umar

 

Dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar PDP Alhaji Atiku Abubakar ya taya al’ummar musulmi na Kasar nan murnar zagoyowar watan da aka haifi fiyayyen halitta Annabi S A W.

 

“A madadin iyalina da tawagata, Ina taya ku murnar wannan lokaci na Maulidi domin tunawa da zagayowar ranar haihuwar Annabi Muhammad SAW” .

 

Kadaura24 ta rawaito Atiku Abubakar ya bayyana hakan ne cikin sakonsa na taya al’ummar musulmi murnar zagoyowar ranar da aka haifi fiyayyen halitta Annabi S A W.

Talla

“A lokacin da muke murna da biki a wannan rana, Ina kira ga dukkan ƴan Najeriya dake gida da waje, da su ɗabbaƙa muhimmancin wannan rana. Rayuwar Manzon Allah SAW na koyar da zaman lafiya, ƙauna da haƙuri, waɗanda halaye ne da ya zama wajibi mu yi aiki da su don zama tare a ƙasa irin tamu”. Inji Atiku Abubakar

 

sanarwa ta Kara da cewa “Kuma a lokacin da muke gaf da yin aiki na tarihi da zai bayyana makomar ƙasarmu, Ina kira gare ku kan ku haɗa hannu waje guda a aikin kuɓutarwa, haɗe kai, sauya fasali da gina Najeriya irin wadda muke mafarkin gani, ƙasar da kowa zai zauna lafiya ba tare da kallon addini, aƙida, yare ko siyasar da yake yi ba”.

 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Majalisar Dokokin Kano ta yi Doka kan masu tufar da yawu da majina a titi

Majalisar Dokokin jihar Kano ta amince da dokar cin...

Sanata Barau zai baiwa dalibai 1,000 tallafin karatu a Kano ta tsakiya da ta Kudu

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau...

Kamfanin Gerawa ya ba da tallafin Kwamfutoci 100 ga al’ummar Gezawa

Daga Abdulmajid Habib Tukuntawa   Kamfanin shinkafa na Gerawa Rice Mills...

Gwamnan Kano ya baiwa maja-baƙin Sheikh Karibullah da wasu malamai muƙami

    Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf ya amince...