Mukaman dana rike a gwamnatoci uku yasa nafi kowanne dan takarar gwamna chanchanta a kano – Dr. Gawuna

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Mataimakin Gwamnan Kano, kuma ɗan takarar Gwamna a jam’iyyar APC, Dr. Nasiru Yusuf Gawuna, ya bayyana kan sa a matsayin wanda yafi duk sauran yan takarar gwamnan Kano saboda kwarewar sa a harkar gwamanti da Kuma jagorancin al’umma.

” Jama’ar Kano su ne za suyi shaida saboda sun san wane ɗan takara ne yake da cancantr ya jagorance su, da taimakon su za mu yi nasara a zaɓen “, in ji shi.

Musa Iliyasu Kwankwaso na cigaba da daka wawaso a cikin NNPP ta Kura Madobi da Garun Malam

Dr. Gawuna ya bayyana haka ta cikin Wani shiri da aka gabatar a gidan talabijin na kasa wato NTA, mai suna “political update”, kamar yadda yake a ƙunshe cikin wata sanarwa da sakataren yaɗa labaran da, Hassan Musa Fagge ya fitar a ranar lahadi .

 

“Wannan gwamantin ta yi ayyuka raya ƙasa da more rayuwa da dama wajen ciyar da jihar gaba “, a cewar Dr. Gawuna.

2023: Takarar Sha’aban Sharada nake goyon baya a ADP Kuma zan bashi gudunmawa har ya ci zabe – Rarara

Yace mukaman da ya riƙe a gwamnatoci guda 3 a Kano da kumu kasancewarsa mataimakin gwamna a yanzu sun sa ya Sami kwarewa da sanin makamar aiki fice da sauran yan takarar na sauran jam’iyyu a Kano.

Mataimakin Gwamnan ya kuma bayyana ɓarakar da sauran jam’iyyun siyasar ƙasar nan ke fama da shi a matsayin ɗaya daga abinda zai tabbatar musu da nasara, ganin yadda APC take tsintsiya maɗaurin ki ɗaya a yanzu.

Dr. Gawuna, wanda yake riƙe da muƙamin mataimakin Gwamnan Kano, ya taɓa riƙe matsayin shugaban ƙaramar hukuma har sau biyu, da na tsohon Kwamishina gona da albarkatun ƙasa sau uku, yanzu haka yana neman kujerar Gwamnan Kano a zaɓen 2023.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kotu a Kano ta hukunta masu shago saboda zubar da shara a kan titi

Kotun tafi da gidanka da ke Kano ta yanke...

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama mata da maza da ke aikata badala

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama mata hudu...

Hukumar Kula da Gidajen Gyaran Hali ta Magantu Kan Batun Sheikh Abduljabbar

Hukumar Gyaran Hali ta Jihar Kano ta bayyana cewa...

Dalilin da ya sa na bar tafiyar Kwankwasiyya – Farouk Lawan

Tsohon ɗan majalisar tarayya, Farouk Lawan, ya bayyana cewa...