Mukaman dana rike a gwamnatoci uku yasa nafi kowanne dan takarar gwamna chanchanta a kano – Dr. Gawuna

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Mataimakin Gwamnan Kano, kuma ɗan takarar Gwamna a jam’iyyar APC, Dr. Nasiru Yusuf Gawuna, ya bayyana kan sa a matsayin wanda yafi duk sauran yan takarar gwamnan Kano saboda kwarewar sa a harkar gwamanti da Kuma jagorancin al’umma.

” Jama’ar Kano su ne za suyi shaida saboda sun san wane ɗan takara ne yake da cancantr ya jagorance su, da taimakon su za mu yi nasara a zaɓen “, in ji shi.

Musa Iliyasu Kwankwaso na cigaba da daka wawaso a cikin NNPP ta Kura Madobi da Garun Malam

Dr. Gawuna ya bayyana haka ta cikin Wani shiri da aka gabatar a gidan talabijin na kasa wato NTA, mai suna “political update”, kamar yadda yake a ƙunshe cikin wata sanarwa da sakataren yaɗa labaran da, Hassan Musa Fagge ya fitar a ranar lahadi .

 

“Wannan gwamantin ta yi ayyuka raya ƙasa da more rayuwa da dama wajen ciyar da jihar gaba “, a cewar Dr. Gawuna.

2023: Takarar Sha’aban Sharada nake goyon baya a ADP Kuma zan bashi gudunmawa har ya ci zabe – Rarara

Yace mukaman da ya riƙe a gwamnatoci guda 3 a Kano da kumu kasancewarsa mataimakin gwamna a yanzu sun sa ya Sami kwarewa da sanin makamar aiki fice da sauran yan takarar na sauran jam’iyyu a Kano.

Mataimakin Gwamnan ya kuma bayyana ɓarakar da sauran jam’iyyun siyasar ƙasar nan ke fama da shi a matsayin ɗaya daga abinda zai tabbatar musu da nasara, ganin yadda APC take tsintsiya maɗaurin ki ɗaya a yanzu.

Dr. Gawuna, wanda yake riƙe da muƙamin mataimakin Gwamnan Kano, ya taɓa riƙe matsayin shugaban ƙaramar hukuma har sau biyu, da na tsohon Kwamishina gona da albarkatun ƙasa sau uku, yanzu haka yana neman kujerar Gwamnan Kano a zaɓen 2023.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Iftila’i: An tsinci gawar wata dattijuwa mai shekaru 96 cikin rami masai a Kano

A ranar Alhamis al’ummar ƙauyen Sarai da ke ƙaramar...

Na riga Kwankwaso shiga harkokin Siyasa – Sanata Barau Jibrin

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, ya...

Jaridun Amurka sun bankado Tsare-tsare uku da sojojin Amurka ke yi don tunkarar Najeriya

Rahotanni daga wasu jaridun Amurka na bayyana cewa rundunar...

Dalibai 22 sun kammala karatu da daraja ta 1 a bikin yaye ɗalibai na farko na Jami’ar Baba-Ahmed Kano

Jami’ar Baba-Ahmed, Kano ta gudanar da bikin yaye ɗalibai...