Daga Zara Jamil Isa
Rukuni na biyu na Maniyatan jihar Kano sun tashi daga filin jirgin saman Aminu Kano zuwa birnin Madina na kasar Saudiyya.
Sakataren zartarwa na hukumar Alhaji Mohammad Abba Danbatta ne ya bayyana hakan yayin wata tattaunawa da manema labarai a Kano.
Ya ce wadanda aka kwaso a zango na biyu sun hada da mahajjata daga karamar hukumar Fagge, ma’aikatan hukumar, malamai, da sauran jami’an hukumar.
Mohammad Abba Danbatta ya lura cewa jirgin ya tashi ne da misalin karfe 8 na safiyar yau Alhamis.
Da yake jawabi ga mahajjatan kafin tafiyarsu, sakataren zartaswar ya umarce su da su kasance jakadu nagari tare da yi musu addu’ar samun zaman lafiya a jihar Kano da kasa baki daya.