Hajjin bana: Rukuni na biyu na Maniyatan jihar Kano sun tashi zuwa kasa mai tsarki

Date:

Daga Zara Jamil Isa

 

Rukuni na biyu na Maniyatan jihar Kano sun tashi daga filin jirgin saman Aminu Kano zuwa birnin Madina na kasar Saudiyya.

 

Sakataren zartarwa na hukumar Alhaji Mohammad Abba Danbatta ne ya bayyana hakan yayin wata tattaunawa da manema labarai a Kano.

 

Ya ce wadanda aka kwaso a zango na biyu sun hada da mahajjata daga karamar hukumar Fagge, ma’aikatan hukumar, malamai, da sauran jami’an hukumar.

 

Mohammad Abba Danbatta ya lura cewa jirgin ya tashi ne da misalin karfe 8 na safiyar yau Alhamis.

 

Da yake jawabi ga mahajjatan kafin tafiyarsu, sakataren zartaswar ya umarce su da su kasance jakadu nagari tare da yi musu addu’ar samun zaman lafiya a jihar Kano da kasa baki daya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...

Idan mu ka rungumi Addu’o’i ba abun da Amurka za ta iya yiwa Nigeria – SKY

Shahararren ɗan kasuwa a Kano, Alhaji Kabiru Sani Kwangila...

Shugaban APC na Kano Abdullahi Abbas ya Magantu Kan Zargin raba Ramat da Kujerarsa

Shugaban jam’iyyar APC na Jihar Kano, Alhaji Abdullahi Abbas,...