Matar wanda a ke zargi da kashe Hanifa ta bada shaida a kansa a kotu

Date:

 

A jiya Alhamis ne Jamila Sani, matar Abdulmalik Tanko, wanda a ke zargi da yin garkuwa da kuma kashe Hanifa Abubakar, ƴar shekara 5 a Jihar Kano, ta bada shaida a kan mijinta.

Tun a zaman kotun na jiha ne lauyan gwamnati, Musa A. Lawal ya gabatar da shaidu guda uku bayan da a zaman kotun na baya Tanko ya nisanta duk tuhume-tuhumen da a ke masa.

Shaidun sun haɗa jami’an ƴan sandan farin kaya, DSS biyu sai kuma ɗan sanda guda daya, wanda shi ne ma wanda ya binciki laifin.

Da a ke mata tambayoyi a zaman kotun na jiya, matar Tanko ta tabbatar da cewa ya kawo Hanifa gidan, inda ba ta fi tsawon kwanaki shida ba.

A cewar matar, da ta tambayi Tanko ko ƴar waye sai ya ce ai ƴar malamar da ke aiki a makarantar sa ne, inda ya ce mahaifiyarta ta samu aiki a Saudi Arebiya shi ne ta tafi Abuja domin cike wasu takardu.

Matar Tanko ɗin ta ƙara da cewa da wasa da wasa sai da Hanifa ta kwana shida a gidan su, sannan da daddare wajen ƙarfe 11 na dare ya ɗauke ta da ga gidan.

Da a ka nuna mata hoton Hanifa, matar Tanko ta tabbatar da cewa ita ce yarinyar da mijin nata ya kawo har ta yi kwanaki 6, har ma ta saba da ƴaƴan ta a gidan.

“Ban san cewa Hanifa ta mutu ba sai da jami’an DSS su ka zo gidan mu, sannan na san halin da a ke ciki,” in ji matar Tanko.

Kadaura24 ta rawaito cewa kawo yanzu dai, an gabatar da shaidu guda takwas a kotun.

Alƙalin kotun, Usman Na-abba, ya umarci a maida waɗanda a ke zargi gidan yari har sai ranar 9 da 10 ga watan Maris za a ci gaba da shari’ar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta dakatar da nuna tallan maganin Gargajiya a Fina-finai da yawo a tituna

A wani mataki na tabbatar da bin ka'idoji tare...

Da dumi-dumi: NNPP ta nemi afuwar Tinubu kan kalaman suka da ake zargin Kwankwaso ya yi masa

  Jam’iyyar NNPP ta nemi afuwar Shugaban kasa Bola Tinubu...

Gwamnatin Kano ta dakatar da Dadin kowa, Labarina, Jamilun jidda da wasu fina-finai 19

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   A kokarinta na tabbatar da ana...

2027: Hon Abdulmumin Jibrin Kofa ya bayyana Matsayarsa kan takarar gwamnan Kano

Daga Zakariya Adam Jigirya   Dan Majalisar tarayya mai wakiltar kananan...