Kotu ta wanke matar Abdulmalik Tanko wanda ake zargi da kisan Hanifa

Date:

Wata kotu a nan Kano ta sallami Jamila Muhammad Sani matar Abdulmalik Tanko wanda ake zargi da kashe ɗalibarsa Hanifah Abubakar.

Kotun Majistare mai Lanba 12 ƙarƙashin mai shari’a Muhammad Jibril ta wanke Jamila a zaman kotun na ranar Juma’a kan zargin da ake mata na ɓoye Hanifa.

Tun da fari dai Lauyan gwamnati Barista Lamiɗo Soran ɗinki ne Lauya mai gabatar da ƙara, kuma kotun ta yi la’akari da bayanan da Jamila ta bayar tare da yin nazari inda ta gano bata da wani laifi a kan batun sace Hanifa Abubakar da kuma kasheta.

Rahotannin sun rawaito Jamila tana cike da farin ciki sakamakon wanke ta da kotun ta yi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta dakatar da Dadin kowa, Labarina, Jamilun jidda da wasu fina-finai 19

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   A kokarinta na tabbatar da ana...

2027: Hon Abdulmumin Jibrin Kofa ya bayyana Matsayarsa kan takarar gwamnan Kano

Daga Zakariya Adam Jigirya   Dan Majalisar tarayya mai wakiltar kananan...

Sarkin Yaƙin Garko, ya ɗauki nauyin dubawa da raba magunguna kyauta ga marasa lafiyar 1400 a Garko

  Sarkin Yaƙin Garko, mai kishin al'umma, kuma ɗan jam'iyyar...

NAHCON ta yi jigilar Maniyatan Nigeria Sama da 24,000 zuwa Saudiyya a kwanaki 10

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Hukumar Kula da aikin hajji ta...