Kotu ta yi fatali da roƙon Muhuyi Magaji na kotu ta hana ƴan sanda su kama shi

Date:

Babbar Kotun Taraiya a Jihar Kano ta yi fatali da buƙatar da dakataccen Shugaban Hukumar Karɓar Ƙorafe-ƙorafe da Yaƙi da Cin-hanci da Rashawa ta Jihar Kano, Muhuyi Magaji Rimingado.

A roƙon da ya shigar gaban kotun, Riminga ya nemi kotun da ta hana kwamitin bincike da majalisar dokoki ta Kano ta kafa, da kuma hana ƴan sanda su bincike shi, tsare shi ko yi masa barazana.

Sannan ya roƙi kotun da ta bada umarnin kowa ya dakata ba tare da ɗaukar mataki kan takardun shaidar lafiya na biyu da a ke zargin yayi amfani da su.

Da ta ke yanke ƙwarya-ƙwaryan hukunci a yau Talata, Mai Shari’a Jane Inyang, ta ce kwamitin bincike da aka kafa da kuma jami’an tsaro suna da iko da doka ta basu na su binciki Rimingado.

Inyang ta kuma yanke cewa babu hurumi na jaddada ko yin watsi da hukuncin da kotu mai hurumi iri ɗaya ta yi da wacce a ka miƙa wa ƙorafi ta yi.

Ta kuma ce kamata ya yi Rimingado ya shigar da ƙorafi a kan yan majalisar dokoki a Babbar Kotun Jiha ba ta taraiya ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi Dangote ya sake rage farashin man fetur a Nigeria

Daga Rahama Umar Kwaru   Matatar mai ta Dangote ta bayyana...

Akwai bukatar kebe rana ta musamman a matsayin ranar tsofaffin dalibai a Kano – Kwamared Waiya

Kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida, Kwamared Ibrahim...

Dubun wani magidanci da ke da’awar bin mamata bashi a Kano ta cika

Daga Aminu Gama   Kotun shari'ar musulunci da ke zamanta a...

Abubuwan da aka tattauna tsakanin Peter Obi da Gwamnan Bauchi Bala Muhammad

Gwamna Bala Muhammed na jihar Bauchi ya ce a...