Majalisar dattawa ta amince da yancin gashin kan harkokin kudi ga Kananan Hukumomi, majalisun Jihohi, da bangaren shari’a

Date:

Daga Khadija Abdullahi Umar
 A ranar Talata ne majalisar dattawa ta kada kuri’ar yin gyare-gyare ga kundin tsarin mulkin kasar na shekarar 1999 wanda ya baiwa majalisun jihohi da na shari’a da kananan hukumomi ‘yancin cin gashin kansu a fannin kudi.
 A kuri’ar da aka kada a zauren majalisar, ‘yan majalisar dattawa 83 ne suka kada kuri’ar amincewa da ‘yancin cin gashin kan harkokin kudi ga majalisun dokoki da na shari’a na Kananan Hukumomin, yayin da Sanata daya ya ki amincewa da hakan.
 Sanatoci 92 ne suka kada kuri’ar amincewa da kudurin yin gyaran fuska ga ‘yancin cin gashin kan kananan hukumomin, yayin da Sanatoci biyu suka ki amincewa.
 Majalisar ta yi watsi da shirin sauya sunan karamar hukumar Barkin Ladi da ke jihar Filato zuwa Gwul.
 A kuri’ar da aka kada, ‘yan majalisar dattawa 67 ne suka kada kuri’ar neman sauya suna, yayin da 28 suka ki amincewa.
 Shawarar ta gaza cika kaso biyu bisa ukun da ake bukata.
 Kafin Amincewa da kowane kudiri , dole ne ya samu rinjaye na kashi biyu bisa uku a zauren majalisar dattawa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Zaizayar kasa: Gwamna Abba gida-gida ya raba diyyar Naira Miliyan 600 A Kano

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir...

Dalilin da ya hana Sarki Aminu Ado Bayero zuwa gidan yari na goron dutse a yau alhamis

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Rahotanni sun tabbatar da cewa Sarkin...

Matakai 3 da gwamnatin Kano ta dauka kan kafafen yada labarai a jihar

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Gwamnatin jihar Kano ta ce a...

Yadda manoma a Kano suka zargi jami’an Civil defense da karbar kudade a wajensu

Daga Umar Ibrahim kyarana   Manoman dajin dansoshiya dake karamar hukumar...