Majalisar dattawa ta amince da yancin gashin kan harkokin kudi ga Kananan Hukumomi, majalisun Jihohi, da bangaren shari’a

Date:

Daga Khadija Abdullahi Umar
 A ranar Talata ne majalisar dattawa ta kada kuri’ar yin gyare-gyare ga kundin tsarin mulkin kasar na shekarar 1999 wanda ya baiwa majalisun jihohi da na shari’a da kananan hukumomi ‘yancin cin gashin kansu a fannin kudi.
 A kuri’ar da aka kada a zauren majalisar, ‘yan majalisar dattawa 83 ne suka kada kuri’ar amincewa da ‘yancin cin gashin kan harkokin kudi ga majalisun dokoki da na shari’a na Kananan Hukumomin, yayin da Sanata daya ya ki amincewa da hakan.
 Sanatoci 92 ne suka kada kuri’ar amincewa da kudurin yin gyaran fuska ga ‘yancin cin gashin kan kananan hukumomin, yayin da Sanatoci biyu suka ki amincewa.
 Majalisar ta yi watsi da shirin sauya sunan karamar hukumar Barkin Ladi da ke jihar Filato zuwa Gwul.
 A kuri’ar da aka kada, ‘yan majalisar dattawa 67 ne suka kada kuri’ar neman sauya suna, yayin da 28 suka ki amincewa.
 Shawarar ta gaza cika kaso biyu bisa ukun da ake bukata.
 Kafin Amincewa da kowane kudiri , dole ne ya samu rinjaye na kashi biyu bisa uku a zauren majalisar dattawa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

An Dauke Shaikh Abduljabbar Daga Gidan Yari na Kurmawa Zuwa Wani Wuri – Yan uwansaba

Wani labari da ke yawo a kafafen sada zumunta...

Majalisu na neman sauya lokacin zabuka a Nigeria

Majalisar Dokoki Ta Ƙasa Ta Gabatar Da Kudirin Sauya...

Kungiyar Lauyoyi yan asalin jihar Kano sun mika korafi ga kasashen Amuruka Ingila da UN kan zargin kisan a Tudun Wada

Kungiyar Lauyoyin Yan Asalin Jihar Kano (National Forum of...

Da dumi-dumi: ASUU ta sanar da ranar da zata fara yajin aiki

Shugabancin Kungiyar Malaman Jami’o’i ta Najeriya (ASUU) ta umurci...